Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Kafa Tarihi: Trump Da Kim Jong Un Sun Hadu


Shugaba Trump da Kim Jong Un a lokacinda sukea hadu a Singapour.
Shugaba Trump da Kim Jong Un a lokacinda sukea hadu a Singapour.

An kafa wani babban tarihi a kasar Singapore, bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya hadu da shugaban Korea ta Arewa, Kim Jong Un domin yin taron koli da aka tsara. Trump, shi ne shugaban Amurka na farko da ke kan mulki da ya hadu da shugaban Korea ta Arewa a tarihin huldar diplomasiyyar kasashen biyu.

A karon farko kuma a wani mataki na kafa tarihi, shugaban Amurka Donald Trump da takwaran aikinsa na Korea ta Arewa Kim Jong Un sun hadu.

Shugabannin biyu sun hadu ne da safiyar yau Talata (lokacin Singapore), inda suka gaisa a gaban totocin kasashen biyu da aka jera a bayansu.

Daga baya kuma sun shiga cikin otel din da taron ke gudana, inda suka fara tattaunawa kan batun da ake tsammanin na kwance damarar makaman nukiliyan Korea ta Arewa ne.

Amma gabanin hakan, shugaba Trump da Kim, sun dan zauna na wani lokaci domin ganawa da manema labarai.

“Lallai ba abu mai sauki ba ne zuwa nan.” Inji Shugaba Kim.

Ya kara da cewa, “zamanin da ya shude ya haifar mana da kalubale kan yadda za a samar da maslaha, amma kuma mun yi hobbasa mun tsallake duk wani shinge, yanzu kuma ga mu a nan yau.”

Shi kuwa shugaban Amurka ya jaddada abin da Kim ya fada ne yana mai cewa, “wannan gaskiya ne.”

Trump ya kara da cewa, “lallai za mu cimma gagarumar nasara, kuma wannan abin alfahari ne, kuma ba na wata tantama, za mu kulla kyakkyawar dangantaka.”

Fadar gwamnatin Amurka ta White House ta ce a daren ranar Talata shugaba Trump zai bar kasar ta Singapore.

Facebook Forum

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG