ZABEN 2023: Hukumar Kula Da Kafafen Yada Labarai Ta Amurka USAGM, Ta Horas Da ‘Yan Jarida Kan Tsare Dokokin Aiki
Hukumar kula da kafafen labarai na ketare ta Amurka wato USAGM, ta hori wakilan kafafen labaru na Najeriya kan yadda za su tsare dokokin aikin jarida idan sun tashi ba da labarai kan yadda za a gudanar da babban zabe har zuwa bayan sanar da sakamako.